News
Jami’an Hukumar DSS Sun Saki Dan Fafutukar Kare Dimokradiyya Zubair A. Zubair
DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Jami’an Hukumar DSS ta saki Zubair, wanda ya kafa ƙungiyar gwagwarmayar dimokuradiyya, wato Take-It-Back Movement (TIB) a Jihar Kano, wanda aka kamashi a ranar Alhamis.
Rahotanni sun bayyana cewa an saki Zubair a Abuja da daddare ranar Juma’a, kuma yana kan hanyarsa ta zuwa Kano.
Sai dai jami’an DSS sun riƙe wayarsa, wadda har yanzu ba a mayar masa da ita ba.
“An saki Zubair jiya da daddare a Abuja. Yana kan hanyarsa ta zuwa Kano a halin yanzu. Amma har yanzu suna riƙe da wayarsa,” in ji wata majiya.
Ƙungiyar TIB, wadda ita ce ta fara bayyana labarin kama Zubair, ta ce dalilan kama shi bai fito fili ba.
Sai dai wasu majiyoyi sun ce an kama shi ne saboda wani rubutu da ya yi a Facebook da ake zargin ya soki gwamnatin Shugaba Tinubu.
Ana yawaitar tsangwamar masu sukar gwamnati a Najeriya daga masu riƙe da muƙamai a matakai daban-daban na ƙasa.
Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin shugabancin Shugaba Bola Ahmad Tinubu, tana fuskantar zarge-zargen tsangwamar ‘yan gwagwarmaya, ‘yan jarida, da kuma waɗanda ke sukar hukumomi.
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
