News
Hisbah Ta Hana Taron Biki Bayan 11 Na Dare
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Hukumar Hisbah ta jaddada cewa har yanzu akwai dokar hana taron biki musamman tsakanin maza da mata, da zarar karfe 11 na dare tayi a jihar Kano.
Mataimakin babban kwamandan Hukumr Hisbah Dr. Mujahiddin Aminudden, ne ya sanar da hakan,ta cikin sakon murya da ya turawa da Jaridar INDA RANKA.
Mahaifiya Da ’Yarta Sun Doke Maza A Gasar Tseren Yada-ƙanin-wani A Kaduna
Ya ce bata gari suna yin amfani da lokutan bukukuwa wajen lalata yan mata.
Hisbah, tace wajibi ne iyaye su rika kula da yanayin yayan su mata a lokutan bukukuwa saboda akwai maza masu yin amfani da lokacin da ake shafewa a wajen taron bukukuwa zuwa tsakar dare don kai yan mata otal da yin lalata dasu.
Hisbah ta kara da cewa a wasu bukukuwan ana iya kaiwa karfe 12 zuwa 3 na dare yan mata basu koma gida ba, kuma Wannan shine babbar hanyar da ake yin lalata da mata.
Haka zalika, Hisbah, ta jihar Kano, ta ce yanzu lokacin bukukuwan kirsimeti da karshen shekara ne don haka su kula da yayan su, da kuma inda suke zuwa da wadanda suke yin ma’amala dasu.
A wani cigaban, Hisbah ta sanar da kama wani Matukin babur mai kafa uku (Adaidaita Sahu) wanda ya samu damar lalata wata yarinya tare da kaita gidajen banza ana lalata da ita.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
