News
Yan Bindiga Sun Hallaka Jami’in Sa-kai, Sun Sace Matan Fitaccen Dan Kasuwa A Kano
Wasu ƴan bindiga sun kai hari a garin Kafin Maiyaki da ke ƙaramar hukumar Kiru, jihar Kano, inda suka kashe wani jami’in sa-kai sannan suka yi garkuwa da matan wani fitaccen ɗan kasuwa a yankin.
Shaidun gani da ido sun ce maharan sun kai samame gidan Alhaji Ibrahim Ahmad Rufai, shugaban ƙungiyar ƴan kasuwar Kafin Maiyaki, inda suka yi awon gaba da matansa zuwa wurin da ba a sani ba.
BBC Hausa Ta Ƙi Karɓar Ajiye Aikin Shugabanta Aliyu Tanko, Ta Dakatar da Shi Tsawon Watanni Uku
A yayin harin, wani ɗan sa-kai da ya yi ƙoƙarin kare al’umma daga farmakin maharan ya rasa ransa.
Wani masani kan tsaro a yankin, Bakatsine, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis ta hanyar wallafa sanarwa a shafinsa na X.
Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa kanharin ba.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
