Connect with us

News

Saudiya ta hana shiga Harami da gajeren wando

Published

on

FB IMG 1646024487172
Spread the love

Daga muslim yunus abdullahi

 

 

Advertisement

Masarautar Saudiyya ta sanar da haramta wa maniyyata sanye da gajeren wando shiga masallatan Harami biyu masu tsarki, wato Masjid al-Haram da ke Makkah da Masjid Al Nabawi a Madina.

Duk wanda aka samu ya saɓa wa wannan sabuwar doka, za a ci shi tarar shi Riyal 200 zuwa 500.

Umurnin na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta fitar, wacce a ka wallafa a shafinta na Twitter na Haramain Syarifain a ranar Juma’a.

Advertisement

A cewar mahukuntan Saudiyya, sanya gajeren wando a masallatai da cibiyoyin gwamnati bayan aiwatar da wannan sabuwar doka ya saɓawa tsarin zamantakewa.

Sai dai gwamnati ta yi karin haske kan cewa mazan da ke sanye da gajeren wando a wani gurin da ba masallaci ba, ba za a ɗauke su a matsayin keta alfarmar sanya tufafi na jama’a ba sai a masallatai.

An shigar da sabbin tarar ne jim kadan bayan ministan harkokin cikin gida na Saudiyya Yarima Abdulaziz Bin Saud Bin Naif ya bayar da sanarwar ga ministocin inda ya bukaci a yi sauye-sauye.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *