Connect with us

News

Ba na nadamar komawa ta APC — Umahi

Published

on

Spread the love

Daga maryam Bashir musa 

 

 

 

Advertisement

Gwamnan Jihar Ebonyi, David Umahi ya ce bai yi nadamar sauya sheƙa zuwa jam’iyar APC ba.

Umahi ya baiyana haka a yau Laraba yayin da ya ke jawabi ga ƴan jam’iya da magoya bayan sa a wani gangamin nuna goyon baya a Abakaliki.

Umahi, wanda ya yi kira da a kwantar da hankula ya tabbatar wa da ƴan jam’iya da masoyansa da su ka halarci gangamin da cewa hukuncin kotun danya cire shi a matsayin gwamna ba tabbatacce ba ne.

Ya kuma nanata cewa bai yi nadamar barin PDP ba , wacce ya ce ba a bin da ta sa a gaba sai ci wa gwamnatinsa dunduniya.

Advertisement

Ya tabbatar da cewa hukuncin kotun ba zai wuce ba a kotun koli, inda ya jaddada cewa shi ne gwamna har yanzu kuma yana nan ya na aikin sa a matsayin gwamna.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *