News
EFCC ta gano gidajen Akanta Janar guda 17 a Landan, Abuja, Legas, Kano da Dubai
Daga maryam bashir Musa
Hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa watau EFCC ta bankado gidajen Akanta Janar na tarayya, Ahmad Idrs, guda goma sha bakwai (17).
Najeriya Na Bukatar Shugabanni Masu Dan Tabin Hankali — Obasanjo
Punch ta ruwaito cewa wani jami’in EFCC wanda ya bukaci a sakaye sunansa yace Idris ya mallaki gidaje a Kano, Lagos, Abuja, Dubai da London
Ya kara da cewa an gani Ahmad Idris ya yi amfani da wasu makusantarsa wajen sayen wadannan dukiyoyi.
Jami’n yace ga dukkan alamu, ya mallakai wadannan dukiyoyin ne yayinda yake Ofis amma bai ayyana cikin takardar hukumar ladabtar da ma’aikata ba kamar yadda doka ta tanada.
Yace “Kimanin gidaje 17 a Kano, Lagos, Abuja, Dubai da London aka bankado mallakinsa. A Abuja, wasu gidajen na manyan rukunin gidaje.”
A cikin makon nan ne dai, hukumar EFCC ta awon gaba da Ahmed Idris wanda take zargin da yin ruf da ciki akan wasu kudade da keangilolin bogi, wanda adadin su ya kai naira biliyan tamanin.
Tuni dai ministar kudi Zainab Shamsuna ta bayyana dakatar da Ahmed Idris daga kan muƙamin sa.
