Connect with us

News

Ganduje ya zargi yan kwankwasiyya da farmakar jama’ar gari ranar Lahadi

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abdullahi Umar Ganduje, tace tana Allah wadai ta farmakin da tawagar kwankwasiyya ta tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, suka kaiwa jama’ar gari a ranar Lahadin da ta gabata, yayin bude ofishin yakin neman zaɓen jam’iyyar NNPP da ke unguwar Sharada a jihar Kano.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai na jihar Kano, kuma mai magana da yawun takarar Gawuna/Garo, kwamared Muhammad Garba, ya bayyana cewa sunyi takaici da abinda ya faru, domin sunyi tsammanin za’ayi yakin neman zaɓe cikin kwanciyar hankali, amma sai suka lura da yadda magoya bayan NNPP suka dauki muggan makamai harda ƙwacen Waya, a cewarsa.

Kwamishinan ya kara da cewa, tuni gwamna Ganduje ya ja hankalin jami’an tsaro akan lamarin, domin su ne masu alhakin tabbatar da zaman lafiya, da kuma tabbatar da cewa kowacce jam’iyyar ta gudanar da yakin neman zaɓenta cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

 

Advertisement

 

 

 

Nassara radio

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending