Connect with us

News

Karin Albashi: Ma’aikatan Jinya Za Su Tsunduma Yajin Aiki A Birtaniya

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

A karon farko cikin shekara 106 da kafa kungiyarsu, ma’aikatan jinya a duk fadin Birtaniya sun bayyana aniyarsu ta tsunduma yajin aiki saboda kin yi musu karin albashi.

Advertisement

 

Rahotanni sun ce kungiyar ta ce zaben jin ra’ayin mambobinta da ta gudanar ya nuna cewa akasarinsu na goyon bayan a shiga yajin aikin a kwanan nan.

Advertisement

 

2023: Zaɓe ba shi da wani amfani, matsawar sai an je kotu ake tabbatar da shugabanni – Lauya Adegboruwa

Advertisement

Ministan Lafiya na Birtaniya, Steve Barclay, ya bayyana yunkurin ma’aikatan a matsayin abin takaici.

 

Advertisement

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar ta ce tsadar rayuwa da tashin farashin kayayyakin da ake fama da su a kasar sun sa mambobinta sun koma rayuwar hannu-baka-hannu-kwarya.

 

Advertisement

“Wannan lokaci ne mai cike da kalubale a tarihin gwagwarmayarmu, kuma fafutukar da muke yi za ta ci gaba yayin yajin aikin da ma bayan kammala shi, har sai an inganta mana sana’a,” inji Sakatariyar kungiyar, Pat Cullen.

 

Advertisement

“Wannan shi ne mataki na karshen da za mu iya dauka. Mambobinmu na cewa tura fa ta kai bango,” inji ta.

 

Advertisement

Ana sa ran yajin aikin zai fara kafin karshen wannan shekarar, kuma za a sanar da ranar fara shi nan ba da jimawa ba.

 

Advertisement

Ma’aikatan dai na neman a kara musu albashi ne da kaso biyar cikin 100 saboda tashin gwauron zabon da farashin kayayyaki ya yi a kasar a ’yan watannin nan.

 

Advertisement

Ma’aikata a bangarorin ayyuka daban-daban na kasar ne suka shiga yajin aiki a kasar daga farkon bazarar bana ya zuwa yanzu. (AFP)

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending