Connect with us

News

Gwamnati Za Ta Lalata Bindigogi 3,000 Da Ta Kwato A Hannun ’Yan Ta’adda

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Ofishin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan Sha’anin Tsaro (NSA) ta hannun Cibiyar Kula da Makamai ta Kasa (NCCSALW), zai lalata bindigogi sama da 3,000 da aka kwace daga hannun ’yan ta’adda a sassan Najeriya.

Cibiyar ta ce an kwace galibin makaman ne a cikin wata 18 da suka gabata a shiyyoyin Arewa maso Yamma da Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas da kuma Arewa ta Tsakiya.

Advertisement

Kamfanoni sun yi karin kuɗin ruwan leda a Najeriya

Da yake yi wa manema labarai karin haske kan batun a Kaduna, Shugaban Cibiyar NCCSALW na Kasa, Manjo-Janar Abba Muhammed Dikko (mai murabus) ya bayyana cewa, an kwace makaman ne a cikin watanni 18 da suka shude.

Ya ce hukumomin tsaro daban-daban kuma daga sassa daban-daban ne suka mika wa cibiyar makaman bayan da suka kama.

Advertisement

Ya kara da cewa, matakin lalata makaman na daga umarnin Shugaba Muhammadu Buhari na inganta tsaro a fadin kasa.

A cewarsa, bindigogi kirar AK-47 da AK-49 da sauransu na daga cikin makaman da za a lalata din.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending