Connect with us

News

Zargin Tsare Dalibi: Aisha Buhari Ta Kulle Shafinta Na Twitter

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Uwar Gidan Shugaban Kasa, Aisha Buhari, ta garkame shafinta na Twitter bayan caccakar da take sha kan zargin dauke wani dalibi da ya yi mata kalaman batanci a shafukan sada zumunta.

Advertisement

 

Wannan na zuwa ne bayan yadda dubban masu amfani da shafukan sada zumunta a Najeriya da ketare ke ta yin fashin baki kan lamarin da ya faru tsakanin Aisha Buhari da dalibin mai suna Aminu Adamu Mohammed da ke Jami’ar Tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa.

Advertisement

 

Zan Ci Gaba Da Faɗawa Shugabanni Masu Mulki Gaskiya – Sultan

Mutane da dama sun bayyana ra’ayinsu kan dauke dalibin, inda wasu ke ganin akwai rashin adalci a lamarin.

Advertisement

 

Wasu kuma na ganin cewar akwai bukatar a bari shari’a ta yi aikinta a kan dalibin da Uwar Gidan Shugaban Kasa ke ganin ya ci zarafinta.

Advertisement

 

Tun da farko dai dalibin ya yi amfani da shafin Twitter wajen wallafa cewar “Su mama an ci kudin talakawa an koshi.”

Advertisement

 

Wasu rahotanni da ba a tabbatar da ingancinsu ba, sun ce wasu jami’an tsaro ne da ake kyautata zaton DSS ne suka yi awon gaba dalibin zuwa Fadar Shugaban Kasa, inda aka dinga jibgarsa, har sai da ya fita daga hayyacinsa.

Advertisement

 

Sai dai bayan abubuwa sun yi kamari, Kungiyar Dalibai ta Kasa (NAN), ta aike da sakon bayar da hakuri ga A’ishan kan cewar ta yafe wa dalibin a matsayinta na uwa.

Advertisement

 

Wannan lamarin dai ya yamutsa hazo, inda wasu ke amfani da damar wajen bayyana bacin ransu musamman, ga gwamnatin APC, wadda wasu ke ganin ta gaza a wasu wurare.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending