Connect with us

News

Kotu Ta Ba Da Belin Masu Barazanar Yada Hotunan Tsiraci

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

 

Advertisement

 

Wata kotun majistare da ke Legas ta ba da umarnin tsare wasu matasa biyu da suka yi barazanar yada hotunan wata mata tsirara a shafukan sada zumunta.
Advertisement

Matasan masu shekaru 23 ana tuhumar su ne da laifin daukar makwabciyarsu hoto tsirara ba tare da saninta ba, sannan suka bukaci ta ba su N200,000 ko su yada ta a kafafen sada zumunta.

Tarayyar Turai ta sanya takunkumi kan mutanen da ke da hannu a rikicin gabashin Kongo

Sai dai aminiya ta rawaito cewa wadanda ake tuhumar sun musanta zargin, kuma Alkalin kotun, Misis B. O. Osunsanmi, ta ba su beli kan N3000,000, da masu tsaya musu da suka mallaki makamancin kudin.

Advertisement

Daga nan ta dage sauraron shai’ar zuwa ranar 6 ga watan Fabrairun shekarar 2023.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending