Connect with us

News

Hisbah Ta Rufe Wuraren Shan Giya Sama Da 100 A Zariya

Published

on

 

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata kungiyar addinin Musulunci mai zaman kanta mai suna Hisbah, ta jagorance garkame wuraren shan giya sama da 100 a Karamar Hukumar Sabon Gari da ke Jihar Kaduna.

 

Advertisement

Dan Majalisar Dokokin Jihar Kaduna mai wakiltar mazabar Sabon Gari, Garba Datti Babawo ne ya tabbatar da hakan, yayin gabatar da hsaidar kammala karbar horo ga ’yan kungiyar su 750 da ya gudana a hedkwatar Karamar Hukumar ta Sabon Gari.

 

Advertisement

Abubuwa 5 Da Ke Hana Waya Saurin Caji

Dan majalisar ya ce tun da Karamar Hukumar take ba ta taba samun sa’ida daga ayyukan badala ba sama da lokacin da aka kafa rundunar ta Hisbah.

 

Advertisement

Daga nan sai Babawo ya ja kunnen dakarun da su tabbatar suna bin dokokin dokoki yayin gudanar da ayyukansu.

 

Advertisement

 

Shi ma da yake nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar ta Sabon Gari, Injiniya Mohammed Usman, ya jaddada kudurin gwamnatinsa na kakkabe yankin daga ayyukan masha’a, ta yadda za a sami yanayin kasuwanci mai kyau tare da bunkasa zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Advertisement

 

Tun da farko sai da Kwamandan rundunar a yankin, Abubakar Auwal ya ce dakarun su 750 sun sami cikakken horo a harkar tsaro kan yadda za su gudanar da ayyukansu.

Advertisement

 

Kwamnadan ya kuma ce 500 daga cikin dakarun maza ne, yayin da 250 kuma mata ne, kuma za su sadaukar da kawunansu wajen hidimta wa al’umma.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Aminiya

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending