News
Dalilin Da Rikicin Zabe Ya Ki Ci Ya Ki Cinye Wa A Najeriya
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Shugabar Kotunan Daukaka Kara ta Kasa Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta ce tarin matsalolin da matakan gudanar da zaben Najeriya ke da shi ne ummul’aba’isin rikice-rikicen a fannin.
Mai shari’a Dongban-Mense ta ce yiwuwar rikice-rikicen ce ta sanya aka kafa kotunan sauraron kararrakin zabe, don warware rigingimun zabe da dangoginsu.
Gwamnan Yobe ya bai wa ma’aikata hutun kwanaki biyu domin tarbar shugaba Buhari
Aminiya ta rawaito cewa Ta ce matukar ana son kawo karshen wadannan fitintinu, to dole sai an gyara tsarin zabe daidai da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 da kuma Dokar Zabe ta 2022.
“A matsayin kotunan daukaka kara na matakin kusa da karshe a shari’a, aikinsu ne kafa irin wadannan kotunan da kuma bude wuraren rajista akalla sati daya kafin gudanar da zaben.
“Haka kuma alhakinsu ne kula da gudanarwar kotunan, bisa jagorancin mai mukamin sakatare”, in ji ta.
Ta bayyana hakan ne a jawabinta na bude taron kara wa juna sani na kwana biyu ga sakatariyar kotun zabe a jiya a Abuja.
-
Opinion6 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion6 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
