News
Dalilin Da Rikicin Zabe Ya Ki Ci Ya Ki Cinye Wa A Najeriya
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Shugabar Kotunan Daukaka Kara ta Kasa Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta ce tarin matsalolin da matakan gudanar da zaben Najeriya ke da shi ne ummul’aba’isin rikice-rikicen a fannin.
Mai shari’a Dongban-Mense ta ce yiwuwar rikice-rikicen ce ta sanya aka kafa kotunan sauraron kararrakin zabe, don warware rigingimun zabe da dangoginsu.
Gwamnan Yobe ya bai wa ma’aikata hutun kwanaki biyu domin tarbar shugaba Buhari
Aminiya ta rawaito cewa Ta ce matukar ana son kawo karshen wadannan fitintinu, to dole sai an gyara tsarin zabe daidai da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 da kuma Dokar Zabe ta 2022.
“A matsayin kotunan daukaka kara na matakin kusa da karshe a shari’a, aikinsu ne kafa irin wadannan kotunan da kuma bude wuraren rajista akalla sati daya kafin gudanar da zaben.
“Haka kuma alhakinsu ne kula da gudanarwar kotunan, bisa jagorancin mai mukamin sakatare”, in ji ta.
Ta bayyana hakan ne a jawabinta na bude taron kara wa juna sani na kwana biyu ga sakatariyar kotun zabe a jiya a Abuja.
-
News5 days ago
Dakarun Soji Cafke Wani Shugaban ’Yan Ta’adda a Kaduna, Sun Kwato Harsasai 300
-
News6 days ago
Dan Takarar Gwamnan Kano a Jam’iyyar AP Ya Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Dan-Shagamu
-
News20 hours ago
Rundunar ‘Yansanda Ta Yi Gargaɗi Gam Da Yiwuwar Kai Hare-hare Makarantu Da Wuraren Ibada
