News
Kotu Ta Aika Da Mai Siyan katin zabe A Kano Gidan Yari
Kotu Ta Aika Mai Siyan katin zabe A Kano Gidan Yari
Alkalin kotun mai lamba 14 da ke Gyadi-Gyadi, Kano karkashin jagorancin Mustapha Datti ya tasa keyar wani matashi dan shekara 45 da haihuwa mai suna Dawakin Tofa, mahaifar Gwamna Ganduje a gidan gyaran hali a Kano.
‘Yan sanda sun kama Tasiu Abdullahi Hayin Hago ne biyo bayan rahoton da al’ummar yankin suka samu bayan an gan shi yana rike da katunan zabe na dindindin guda 29 a makon jiya.
Jaridar blazon ta rawaito cewa Ba a bayar da belin Tasiu ba saboda lauyoyin INEC sun yi watsi da bukatar.
Don haka Alkalin kotun Mai shari’a Datti ya tura wanda ake zargin zuwa gidan yari tare da dage sauraron karar zuwa ranar Talata 31 ga watan Janairu domin sauraren karar.
Jam’iyyar adawa ta NNPP ta bayyana wannan ci gaban a matsayin wani gagarumin nasara da aka samu wajen tsaftar zabukan 2023 daga duk wani abu na Sayen Kuri’a.
A wata sanarwa dauke da sa hannun babban mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben NNPP na jihar Sanusi Bature Dawakin Tofa, jam’iyyar ta zargi jam’iyyar APC mai mulki da yin yunkurin yi wa jam’iyyar zagon kasa a zabe mai zuwa ta hanyar bata wa ‘yan kasa hakkinsu ta hanyar siyan katin zabe mai zuwa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
