Connect with us

News

Allah Ya Yi Wa Limamin Jere Rasuwa

Published

on

 

Allah Ya yi wa limamin Jere da ke Karamar Hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, Malam Adamu Usman, rasuwa a wannan Lahadin.

 

Adamu, ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya, kamar yadda daya daga cikin iyalansa, Abbas Bello Ja’afar ya shaida wa Aminiya.

An kama wani dan kasuwa da Miyagun Kwayoyi mai nauyin kilogiram 9.40 a filin jirgin saman Legas

 

Ya ce mahaifin nasu ya rasu bayan jinyar sati daya, kuma an yi jana’izarsa bayan sallar Azahar kamar yadda Addinin Musulunci ya tanada.

Advertisement

 

Ya rasu ya bar ‘ya’ya da jikoki da dama ciki har da zababben Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Lawal Adamu Usman da kuma Durbin Jere, Alhaji Aminu Adamu, ma’aikaci a Muryar Najeriya (VON).

 

Malam Adamu ya rasu yana da shekara 77 a duniya.

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending