Connect with us

Uncategorized

NNPP ta bukaci a soke zaben gwamnan Borno

Published

on

 

Jam’iyyar NNPP ta bukaci Hukumar INEC ta soke zaben Gwamnan Jihar Borno na ranar Asabar, ta gudanar da sabo.
NNPP reshen Jihar Borno ta yi kiran ne saboda rashin sanya sunanta da na dan takararta, Umar Alkali Nasko, a kan takardar kada kuri’a a zaben.
Shugaban NNPP a jihar, Barista Mohammed Mustapha, ya ce babu yadda za a yi su gama bata lokaci wajen yin yakin neman zabe, su gama kashe kudi, amma hukumar ta ki sanya sunan a jam’iyyar ko na dan takarar a takardar kada kuri’a.

Advertisements
Advertisements

Don haka ya ce za su dauki matakin ahari’a domin tabbatar da ganin hukumar ta soke zaben.

Advertisements

INEC Ta Wallafa Sakamakon Zabe 66,600 A Shafin IRev

Amma a nasa bangaren, kakakin INEC a jihar, Abba Liberty, ya ce hukumar ba ta san da zaman dan takarar gwamnan NNPP a jihar ba, saboda ya yi lattin dawo da takardar tsayawarsa takara. Kamar yanda aminiya ta rawaito

Advertisements
Advertisements
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending