Connect with us

News

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Rufe Filin Jirgin Saman Abuja 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

An rufe filin tashi da saukar jiragen sama na Nnamdi Azikiwe dake Abuja na wani dan lokaci sakamakon lamarin da ya rutsa da wani jirgin Max Air.

Advertisement

 

Jaridar indaranka yadda wani jirgin saman Max Air ya yi hatsari a filin jirgin Abuja da yammacin Lahadi.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Jirgin mai lamba B737 mai lamba 5N-MBD ya samu matsala a lokacin da ya sauka, kamar yadda wani bincike na farko da hukumar binciken haddurar jiragen sama a Najeriya ta fitar ya nuna.

Advertisement

 

Daily Trust ta rawaito cewa Jirgin na da fasinjoji 144 da ma’aikata shida a cikinsa. Ya kuma taso ne daga garin Yola na jihar Adamawa kan hanyar zuwa Abuja ranar Lahadi.

Advertisement

 

Sakamakon lamarin dai an karkatar da dukkan jiragen da ke kan hanyar zuwa filin jirgin na Abuja.

Advertisement

 

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, yanzu jirgin na tsaye a kan titin jirgin, wanda hakan ya sa wasu jiragen ba su iya amfani da titin wajan sauka.

Advertisement

 

Hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta kasa (FAAN) da hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya NAMA, sun tabbatar wa wakilin majiyar mu cewa, an rufe filin jirgin na dan wani lokaci har sai an dauke jirgin daga kan titun.

Advertisement

 

Da misalin karfe 7:40 na yammacin ranar Lahadi, kungiyoyin agaji na ci gaba da kokarin kau da jirgin daga wajan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending