News
Ma’aikatan Lafiya Sun Janye Yajin Aiki
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ma’aikatan lafiya na Najeriya sun janye yajin aikinsu na kwana 12 bayan wata ganawa da suka yi da shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu a jiya Litinin.
Ƙungiyar ma’aikatan ta JOHESU, wadda ta yi ganawar da shugaba Tinubu, ta ce ta yanke shawarar janye yajin aikin ne domin bai wa gwamnati wa’adin mako uku domin shawo kan matsalolin da suke fuskanta.
Mataimakin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Dr Obinna Ogbonna ya ce “an samu ci gaba” a tattaunawar da suka yi da shugaban ƙasa.
“Amincewa tamkar abu ne mai haɗari, amma tunda a yanzu muna magana ne da sabon shugaban ƙasa, wanda da kansa ya roƙi mu ba shi lokaci, ya kamata mu ba shi.
“Bayan kwanakin 21 za mu duba inda ake sannan mu ɗauki mataki na gaba.” in ji Dr Obinna
Ma’aikatan lafiyar dai na nema ne a yi watsi da tsarin biyan albashi na bai-ɗaya, da biyansu alawus-alawus ɗin aiki, da sake duba shekarun yin ritaya da dai sauran su.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
