Connect with us

News

Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Bukatar Hana Jami’an Gwamnati Neman Lafiya A Kasashen Waje

Published

on

Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Bukatar Hana Jami'an Gwamnati Neman Lafiya A Kasashen Waje

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Kotun daukaka kara ta Nijeriya ta yi watsi da bukatar hana jami’an gwamnati fita kasashen waje don neman lafiya, bukatar da babban lauya kuma ɗan gwagwarmaya, Femi Falana (SAN), ya shigar.

Advertisement

Falana ya daukaka karar ne bayan da babbar kotun jihar Lagos da ke Ikeja ta ki amincewa da bukatar da ke neman tilastawa gwamnatin tarayya ta gyara asibitocin cikin gida, tare da dakatar da jami’an gwamnati daga tafiya kasashen waje don neman lafiya.

Yadda Faɗuwar Farashin Gas Din Girki A Kano Ya Jawo Dogon Layi A Lokacin Azumi

Babban lauyan ya bayyana cewa irin wannan mataki zai tilasta wa gwamnati maida hankali kan inganta harkar lafiya a cikin gida, domin amfanin ‘yan kasa gaba ɗaya.

Advertisement

Sai dai kotun daukaka kara ta yi watsi da bukatar, tana mai bayyana cewa ba ta da hurumin hana mutum walwala ko yancin neman lafiya a duk inda ya ga dama.

Falana dai na daga cikin manyan ‘yan gwagwarmaya da ke fafutukar ganin an gyara asibitocin Nijeriya domin rage dogaro da kasashen waje wajen kula da lafiyar jami’an

Advertisement

gwamnati.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending