News
Hijira: Gwamnatin jihar Kano ta ayyana gobe Laraba 19 ga watan Yuli a matsayin ranar hutu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin jihar Kano ta ayyana gobe Laraba 19 ga watan Yuli a matsayin ranar hutu domin murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1445.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai Baba Halilu Dantiye fitar a yau.
Sarkin Musulmi,Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar Ya Sanar Da Sabuwar Shekarar Musulunci
Gwamnan wanda ya taya al’ummar musulmin duniya murnar shigowar sabuwar shekara ta Musulunci, ya kuma bukaci ma’aikatan gwamnati da sauran al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya kawo mana zaman lafiya da kwanciyar hankali tare da bunkasar tattalin arzikin jiharmu da kasa baki daya,
Gwamnan ya kuma yi kira ga al’umma da su rika gudanar da rayuwarsu bisa koyarwar addinin Musulunci tare da yin kyawawan dabi’u na kyautatawa da soyayya da kuma hakuri da juna kamar yadda Annabinmu Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi misali da shi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
