Connect with us

News

Hijira: Gwamnatin jihar Kano ta ayyana gobe Laraba 19 ga watan Yuli  a matsayin ranar hutu

Published

on

ABBA KABIR YUSUF

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Gwamnatin jihar Kano ta ayyana gobe Laraba 19 ga watan Yuli  a matsayin ranar hutu domin murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1445.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai Baba Halilu Dantiye  fitar a yau.

Sarkin Musulmi,Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar Ya Sanar Da Sabuwar Shekarar Musulunci

Gwamnan wanda ya taya al’ummar musulmin duniya murnar shigowar sabuwar shekara ta Musulunci, ya kuma bukaci ma’aikatan gwamnati da sauran al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya kawo mana zaman lafiya da kwanciyar hankali tare da bunkasar tattalin arzikin jiharmu da kasa baki daya,

Gwamnan ya kuma yi kira ga al’umma da su rika gudanar da rayuwarsu bisa koyarwar addinin Musulunci tare da yin kyawawan dabi’u na kyautatawa da soyayya da kuma hakuri da juna kamar yadda Annabinmu Muhammadu Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi misali da shi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending