News
Motoci Makare Da Kaya Sun Makale A Kan Iyakar Najeriya Da Jamhuriyar Nijar
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Motocin da ke cike da kaya da ke shiga Nijar a halin yanzu sun makale a garin Jibia da ke kan iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar.
Hakan na zuwa ne bayan da gwamnatin tarayya ta rufe dukkan iyakokin kasa da jamhuriyar Nijar bayan hambarar da gwamnatin Mohamed Bazoum da sojoji suka yi.
Gwamnan jihar Zamfara ya jaddada aniyar gwamnatinsa na magance matsalolin tsaro da ke addabar jihar
Wani dan jarida da ke kan iyaka a ranar Juma’a ya kirga motoci sama da 30 da aka jera a bangarorin biyu na babbar hanyar daga jamhuriyar Nijar
Premium Times ta ruwaito cewa kuma Akwai manyan motoci da aka jera a kan titin daga bangaren Najeriya, da fatan a ba su izinin shiga jamhuriyar Nijar
Mukaddashin kwanturolan hukumar kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce ba za a bari motocin su shiga ko fita ba a yanzu
Muna da manyan motocin da ke zuwa daga Najeriya wadanda ba za su iya zuwa wani bangaren (Jamhuriyar Nijar) ba
Da yawa daga cikinsu suna cikin Katsina idan za ku iya kunna kyamararku, za ku ga abin da muke da shi ma a can inji wani direba da ya Tattauna da yan jarida
Akwai direbobi da mataimaka da dama zaune a karkashin wata bishiya da ke daf da inda aka ajiye motocin
Muna cikin wani mawuyacin hali. Na zo nan ne kafin a rufe iyakar a hukumance amma kafin in samu izini, sai (hukumomin kan iyaka) suka ce sun samu sigina daga Abuja na rufe dukkan iyakokin inji wani direban da ya makale a bakin iyakar
Ya ce ya kashe duk kudin cin abincinsa saboda ranar Juma’a ce kwana na hudu da yayi a kan iyaka
Wani direban da ya makale, ya ce zai yaba idan kasashen biyu suka kawo karshen lamarin
