News
kungiyar kwadago ta NLC Ta Janye Shirinta Na Fara Yajin Aiki
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI.
A halin yanzu, Ba lallai ba ne gamaiyar kungiyoyin kwadago su dauki matakin tafiya yajin aiki daga ranar 14 ga watan da muke ciki, kamar yadda suka sanar tun da farko.
Hakan ya biyo matakin da gwamnatin taraiyya ta dauka, na janye karar data kai ‘yan kwadagon, bisa zarginsu da kin mutunta umarnin kotu, bayan zanga-zangar nuna adawa da tsadar rayuwa da suka yi a Larabar makon jiya.
Gwamnan jahar Kano Ya Kara Nada Mutane 42 A Matsayin Masu Temaka Masa
Shugaban kungiyar kwadago na kasa, Kwamared Joe Ajaero ne ya tabbatar da matakin a daren jiya, yayin wata hira da aka yi dashi a gidan Talabijin na channels.
Idan ba a manta ba a makon jiya ne, gwamnatin taraiyya ta maka kungiyar kwadago gaban kotu, bisa zarginsu da kawo wargi ga umarnin da Kotu ta bayar tun da farko na hana su yin zanga-zanga, Wanda hakan yasa kungiyoyin baiwa gwamnatin taraiyya wa’adin kwanaki 10 data janye karar ko kuma su shiga yajin aiki.
Sai dai Shugaban kungiyar kwadago na kasa, ya tabbatar da cewar gwamnatin taraiyya ta janye karar, kamar yadda aka aike masu da wasika da tsakar ranar jiya.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
