News
Buhari ya jajanta wa iyalan sojojin da aka kashe a Neja.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI.
Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa kan mutuwar sojojin ƙasar nan da aka kashe a wani ƙwanton-ɓauna da ‘yan bindiga suka yi musu tare da faɗuwar wani jirgin helikofta na soji a jihar Neja.
Cikin wani saƙon Twitter da tsohon shugaban ƙasar ya wallafa ya ce ya kaɗu da hatsarin jirgin helikoftan, bayan da kuma aka yi wa waso sojojin ƙaar kwanton-ɓauna.
“Ina miƙa soƙon jaje ga iyalan mamatan. ina kuma yi wa waɗanda suka jikkata addaua’r fatan samun lafiya”.
Buhari ya kuma aike da saƙon ta’aziyyarsa ga shugaban Najeriya Bola Tinubu, da rundunar sojin ƙasar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
