Connect with us

News

Gwamnatin Legas ta haramta sayarwa da amfani da robar ‘take-away’

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Kwana kaɗan bayan Gwamnatin Jihar Legas ta kafa dokar hana sarrafawa, sayarwa da zuba abinci cikin robar ‘take-away’, yanzu haka an bayar da umarnin a damƙe duk wanda aka ƙara gani ya na sayar da robar ta zuba abinci.

Advertisement

Haka umarnin ya haɗa da duk wanda ya zuba wa kwastomomi abinci a cikin robar da kuma wanda ya sayi abinci aka zuba masa a ciki.

Yan Majalisar Filato Da Kotu Ta Kwace Kujerunsu Sun Lashi Takobin Dowawa Bakin Ai

Sanarwar ta fara ne da bada umarnin a garƙame duk wata masana’antar da aka yin robobin na zuba abinci da kuma manyan dillalan da ke sayarwa lodi-lodi.

Advertisement

Premium Times ta ruwaito cewa Kwamishinan Tsaftace Muhalli na Jihar Legas, Tokumbo Wahab ne ya sanya wa sanarwar hannu da kan sa, a wata takardar da aka fitar ranar Lahadi.

Sanarwar ta umarci Hukumar Tsaftace Jihar Legas, wato LAWMA da Dakarun Yaƙi da Rashin Ɗa’a su gaggauta su fara damƙe duk wanda ya karya wannan doka.

Advertisement

Wahab ya ce abin takaici ne ƙwarai yadda waɗannan robobi suka cushe magudanun ruwa, sannan kuma a kullum gwamnati na asarar maƙudan kuɗaɗe wajen yashe magudanan ruwan.

Ya ce mafi yawan sharar da jami’an LAWMA ke fama da ita kan tituna da gefen titinan a kullum, duk robobin abinci ne na ‘take-away’.

Advertisement

 

Ya ce daga yau Gwamnatin Jihar Legas ba za ta zuba ido ya riƙa zubar da ƙazanta ba, sannan a bar ta da kashe maƙudan kuɗaɗe wajen tsaftace gari.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending