Connect with us

News

Kasar Burkina Faso ta sake dakatar da wasu kafafen yada labarai

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Burkina Faso ta sake dakatar da wasu kafafen yada labarai daga yada shirye-shiryensu a kasar, sakamakon fitar da rahoton hukumar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch, da ta zargi sojojin kasar da yi wa wasu mutanen karkara fararen hula 223 kisan gilla.

Advertisement

DW ta ruwaito cewa Kafafen yada labaran da dakatarwar ta yanzu ta shafa sun hada da Deutsche Welle da ke nan Jamus, da jaridar Faransa ta Le Monde, da Quest-France, sai jaridar Guardian ta Burtaniya da kamfanonin dillancin Afirka na APA da kuma Ecofin.

Hukumar NDLEA Ta Kama Wani Fasinja Ɗauke Da Kwayar Tramadol 4,000 A Filin Jirgin Sama 

Channelstv ta ruwaito cewa Burkina ta fara dakatar da BBC da VOA, da kuma gidan talabijin din Faransa na TV5Monde.

Advertisement

Rahoton na Human Rights Watch ya zargi sojojin Burkina Faso da hallaka fafaren hular 223 a cikin watan Fabarairun da ya gabata, bisa zarginsu da hada baki da ‘yan ta’adda

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending