News
Wike Ya Dakatar Da Sakatare Janar Na Hukumar FCDA Har Sai Baba Ta Gani
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT) Nyesom Wike, ya dakatar da Injiniya Shehu Hadi Ahmad, Sakatare Janar na Hukumar Raya Babban Birnin Tarayya (FCDA), har sai baba ta gani.
Lere Olayinka, Mataimaki na Musamman kan Sadarwar Jama’a da Sabbin Kafofi Labarai ga Ministan ne, ya bayyana hakan cikin wata gajeriyar sanarwa a ranar Alhamis.
A cewar Olayinka, dakatarwar Ahmad ta fara aiki nan take.
Ko da yake ba a bayyana dalilin wannan mataki ba, “an umarci Sakatare Janar da aka dakatar da ya mika mulki ga Daraktan Ayyukan Injiniya na FCDA.”
Advertisements
