News
Ƴan Bindiga Sun Sace Matar Dagaci Da Diyarsa A Kaduna
Wasu ƴan bindiga sun sace matar Dagacin Aboro da ke Ƙaramar Hukumar Sanga a Jihar Kaduna, Harira Abdullahi, da kuma diyarsa, Maryam Suleiman Galadima.
lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:36 na dare a ranar Lahadi, lokacin da ƴan bindigar suka shigo gidan Dagacin Aboro, Alhaji Shuaibu Suleiman Galadima, suka kuma tafi da matar da diyarsa.
Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida LEADSHIP cewa bayan da aka sace su, mazauna yankin suka taru domin bin ƴan bindigar da nufin ceto su.
“Mun bi su cikin daji, amma da suka gan mu sai suka bude mana wuta. Sun kashe ɗaya daga cikinmu, Umar Abdullahi, sannan suka jikkata wani Suleiman, wanda yanzu haka yana asibiti ana kula da shi,” in ji shi.
An binne mamacin bisa tsarin Musulunci a daren ranar da abin ya faru.
Mazaunin ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro da su gaggauta ɗaukar matakin ceto matar da diyarta, da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin.
Kokarin jin ta bakin rundunar ’yan sandan jihar Kaduna ya ci tura, domin kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, bai amsa kira ko saƙonnin da aka aike masa ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Akwai yawaitar hare-haren garkuwa da mutane a wasu sassan jihar Kaduna, musamman a yankunan karkara, abin da ke kara tsananta tsoro da fargaba a tsakanin al’umma.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
