Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Sace Masu Kai Amarya A Zamfara

Published

on

‘Yan bindiga sun sace mata kimanin 27 da ke rakiyar kai wata amarya a kauyen Kumi a karamar hukumar Maru da ke jihar Zamfara.

Rahotanni sun ce ‘yan bindiga ne suka tare su a hanya suka kuma yi awon gaba da su ba tare da bata lokaci ba.

Advertisement

‎APC Na Samun Gagarumar Goyon Bayan Kano Arewa Saboda Jiga-Jigan Siyasa Uku

Wani mazaunin yankin ya shaida wa sashen Hausa na BBC cewa, matan sun taso ne domin halartar wani bikin aure da ke wani kauye a makwabtaka da nasu, sai dai suka fada hannun masu garkuwa da mutane a tsakiyar hanya.

A wani lamari makamancin haka, wasu mutane 19 ne aka sace a garin Galadi da ke karamar hukumar Tsafe, inda maharan suka kai farmaki da dare. Wasu daga cikin mazauna yankin sun samu raunuka a yayin harin.

Advertisement

Wadannan hare-hare na baya-bayan nan sun sake tayar da hankalin al’umma a yankunan, inda jama’a ke kara shiga halin fargaba da damuwa.

Jihar Zamfara na daga cikin wuraren da ke fama da matsalar tsaro, musamman a yankunan karkara, inda ‘yan bindiga ke ci gaba da kai hare-hare, sace mutane da kuma tilasta wa jama’a biyan kudin fansa.

Advertisement

 

DAILY POST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending