News
Kotu Ta Tura Matasa Gidan Yari Kan Yunkurin Hana Zance A Kano
Wata kotun shari’ar Musulunci da ke Kofar Kudu a jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Shamsuddeen Ado Abdullahi Unguwar Gini, ta tura wasu matasa biyu gidan yari bisa zargin kai hari kan wani saurayi da ya je yin zance a unguwar Ja’en da adda.
Wadanda ake zargin, Usman Rabi’u Usman da Aliyu Rabi’u Usman, na fuskantar tuhuma ne daga Kungiyar Ci Gaban Al’ummar Ja’en, wadda ta shigar da karar bisa zargin cewa matasan sun ɗauki doka a hannunsu tare da kafa dokar hana yin zance a unguwar.
Lauyar gwamnati, Barista Aliya Aminu Yargata, ce ta gabatar da kara a gaban kotun, inda ta karanta musu tuhumar. Duk da cewa sun musanta laifin, lauyar ta nemi lokaci domin gabatar da shaidu a gaba.
Lauyan wadanda ake kara, Barista Jamilu Ja’afar, ya roki kotun da ta ba su beli, amma Mai Shari’a bai amince da bukatar ba.
Kotun ta umarci a tsare su a gidan yari har zuwa ranar 22 ga watan Mayu, domin ci gaba da sauraronshari’ar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
