News
Gwamnatin Tarayya Za Ta Kashe N1.5trn Don Gyara Layin Dogo Mai Amfani Da Lantarki A Kano
Gwamnatin Tarayya ta ce za ta kashe Naira tiriliyan 1.5 wajen gyara layin dogo jirgin ƙasa mai amfani da lantarki a Kano.
Shugaban Kwamitin Ƙasafin Kuɗi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Abubakar (Bichi), ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis.
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Yawaitar Hare-haren ’Yan Bindiga A Zamfara
Ya ce aikin, wanda darajarsa ta kai dala biliyan ɗaya, zai rage cunkoson ababen hawa, ya inganta zirga-zirgar mutane da kaya, tare da ƙara wa tattalin arzikin jihar ƙarfi.
“Wadanda suka yi tafiya zuwa ƙasashen Turai da Asiya sun ga irin waɗannan ayyuka da tasirin su ga ci gaban birane. A nan Kano, wannan aikin zai haɓaka tattalin arziki matuƙa idan an kammala shi,” in ji Bichi.
Bichi ya ce maganar cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba ya nuna kulawa ga Arewacin Najeriya ba ta da tushe. Ya ce shugaban ƙasar ya kaddamar da ayyuka da dama a yankin, ciki har da gyaran manyan tituna da harkokin sufuri, kiwon lafiya, noma da tsaro.
