Connect with us

News

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Mataimakin Gwamnan Kano Kan Dakatar Da Shirin Tsige Shi

Published

on

images (9)
mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo,

Wata Babbar Kotun Tarayya ta ki amincewa da bukatar neman umarnin wucin gadi da mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya gabatar domin dakatar da shirin tsige shi da majalisar dokokin jihar Kano ta fara.

Jaridar Inda Ranka ta rawaito a hukuncin da mai shari’a S.M. Shaibu ya yanke a ranar 25 ga Maris, 2026, kotun ta bayyana cewa mai neman umarnin bai cika sharudan da ake bukata ba domin a ba shi wannan kariya ta gaggawa.

Advertisement

Haka kuma kotun ta umurce shi da ya mika takardun shari’ar ga wadanda ake kara domin su samu damar mayar da martani yadda ya kamata.

Tun da farko dai, majalisar dokokin jihar Kano ta samu wani umarni na wucin gadi daga kotu a ranar 11 ga Maris, 2026, wanda ya hana mataimakin gwamnan daukar duk wani mataki da zai kawo cikas ga aikin majalisar, musamman dangane da ikon da kundin tsarin mulkin Najeriya ya ba ta karkashin sashe na 188.

Advertisement

 

Karin bayani na nan tafe…

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending