News
El-Rufa’i Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Da Ta Gaggauta Cire Tallafin Man Fetur.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta cire tallafin man fetur.
Ya yi wannan kiran ne a wani taron masu ruwa da tsaki da ke gudana a Abuja.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, a lokacin da a ka tambayi gwamnan, wanda ke jawabi a zagayen tattauna wa a taron, kan ko me ya kamata gwamnati ta sa gaba, sai ya ce, “a cire tallafin man fetur nan take.
El-Rufai ya bayyana cewa gwamnonin jihohi 36 da jami’an gwamnatin tarayya, a majalisar tattalin arzikin kasa, sun amince da cire tallafin man fetur a watan Satumban 2021.
Ya bayyana mamakin sa da yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kasa aiwatar da wannan kuduri, duk da tsananin matsin tattalin arziki da tallafin ya janyo wa kudaden gwamnati da kuma almundahana da ke tattare da hakan.
A cewarsa, gaskiyar yadda ake tafiyar da tallafin, wanda ya kamata a ce gwamnatin tarayya ta kawo karshen sa tun kafin yanzu ya kasance cikin shakku.
Gwamnan ya kuma ce, Majalisar Tattalin Arziki ta Kasa, NEC, ta yi hasashen cewa, idan ba a cire tallafin ba, lokaci zai zo da kamfanin man fetur na ƙasa, NPL, zai ce an kashe daukacin kudaden da kasar ke samu a duk wata wajen bayar da tallafi.
Ya ce: “Masu tsara kundin tsarin mulkin mu sun yi hasashen cewa domin tattalin arzikin ya yi aiki yadda ya kamata, ya kamata a samu daidaito tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi.
“Don haka ne aka kafa Majalisar Tattalin Arziki ta Kasa, inda Mataimakin Shugaban Kasa ya zama Shugaba. Dukkanin gwamnoni 36 mambobi ne da wasu jami’an gwamnatin tarayya kamar ministan kudi.
“A karkashin wannan gwamnatin, kusan duk wata muna haduwa a addini, domin tattalin arzikinmu daya ne kawai,” in ji shi
