Connect with us

News

Ba a kai wa Mai Mala hari ba – Gwamnatin Yobe

Published

on

 

Gwamnan jihar Yobe da ke arewacin Najeriya Mai Mala Buni ya tsallake rijiya da baya a wani hari da aka kai masa yayin yaƙin neman zaɓe a shiyyar Gashua da ke ƙaramar hukumar Bade.

Advertisement

 

Sai dai gwamnatin jihar Yobe ta musanta Ikirarin tana cewa sai da gwamna ya bar wurin hayaniya ta ɓarke.

Advertisement

Manchester City ta doke Aston Villa ta koma matsayinta na biyu

Amma gidan Talabijin na ChannelsDubban magoya bayan APC ɗin ne da suka je yakin neman zaɓen suka riƙa yi wa gwamnan ihu suna cewa “ba ma yi, ba ma son Mai Mala Buni”.

 

Advertisement

An fara rikicin ne lokacin da gwamnan zai miƙa tuta ga ‘yan takarar APC gabanin zaɓen 2023, kawai sai aka fara jifa da dutse da wasu abubuwan na daban.

 

Advertisement

Sai da aka fitar da Gwamnan daga taron tare da taimakon jami’an tsaro.

 

Advertisement

Yana yin dai haka ya tilastawa gwamnan da magoya bayansa barin yankin tare da komawa Damaturu ba tare da shiri ba.

 

Advertisement

Mamman Mohammed wanda shi ne daraktan kula da kafafen yaɗa labari ya ce babu wani abu mai kama da wannan da ya faru.

 

Advertisement

“Mambarin da ake gudanar da taron ne ya cika, lokacin da Sanata Ahmed Lawal ke bayani, sai aka ce kowa ya sauka kada ya ƙarye, har gwamna da shi sanata.

 

Advertisement

“Dalilin barin wurin taron da wuri kenan. Muna zuwa wani gidan mai muka ji rikici ya ɓarke tsakanin mabiya jam’iyyar tamu,” in ji Mamman.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending