News
Fargabar Fuskantar Fari Ta Tilastawa Manoman Jihar Borno Shiryan Addu’ar Rokon Ruwa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Yayinda damunar bana kecigaba da kankama manoma a birnin Maiduguri na jihar Borno na shirye-shiryen gudanar da addu’o’i na musamman kan jinkirin saukar ruwan sama a jihar dake arewa maso gabashin Najeriya.
Al’amarin ya shafi manoma da galibinsu suka fito daga yankunan arewaci da tsakiyar jihar, inda suka ce suna son a hada kai ne domin neman taimakon Allah kan matsalar.
Yan Damfara Na Karbar Kudin ‘Wasu Masu Son Zama Ministoci – Ibrahim Kabir Masari
Daya daga cikin manoman mai suna Ibrahim Ali ya koka da yadda suke ganin hadari kamar za a yi ruwan sama amma bayan wani lokaci sai ayi iska mai karfi hadarin ya washe.
Arewa radio ta rawaito cewa Majalisar masarautar Borno, tace tana goyon bayan addu’o’in.
A wata sanarwa da ta fitar, Majalisar tace ta hada kan jama’a domin gudanar da addu’o’in rokon ruwan sama na musamman da aka shirya gudanarwa a yau Litinin 17 ga watan Yuli 2023 a dandalin Ramat da ke Maiduguri babban birnin jihar ta Borno.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
