Connect with us

News

SUDAN:Ana ci gaba da luguden wuta a wasu yankuna na kasar Sudan

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN

A kasar  Sudan ana ci gaba da luguden wuta a birnin Khartoum da ma yankin yammacin Dafur a cewar shaidun gani da ido, duk da yunkurin kawo karsehn rikicin da kashen duniya ke yi.

Wani mumunan hari da aka kai ta sama a garin Ombada mai yar tazara da birnin Khartoum, ya yi sanadiyar rayukan mutane 5 yayin da wasu 17 suka jikkata.

Wane Mataki Shari’ar Zaben Gwamnan Kano Ke Ciki ?

Masu aikin ceto na ci gaba da neman mutane da suka makale a baraguzen gine-gine, lamarin da ya sa ake ganin adadin wadanda suka mutu ka iya karuwa.

Ya zuwa yanzu, sama da mutum dubu uku ne rikicin na Sudan mai tushe da batun shugabanci suka rasa rayukansu, a cewar wata kungiya mai tattara bayanan yaki, amma kuma wasu na ganin adadin ya zarta haka.

A jiya Asabar ne aka koma teburin tattaunawa a tsakanin sojojin gwamnati da na dakarun RSF a birnin Jeddah na kasar Saudiyya. Zaman da kawo yanzu babu rahoto a kan yadda ya kaya, a baya an yi irinsa ba tare da cimma matsayar kawo karshen yakin ba.

Advertisement

DW

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending