Connect with us

News

Matashi ya shaƙe mahaifiyarsa har ta mutu

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

 

Advertisement

Wani matashi ɗan shekara 32, mai suna Samson Sikiru,ya shaƙe mahaifiyarsa har ta mutu a garin Ijebu Ode da ke jihar Ogun.

Mai magana da yawun ƴan sandan jihar, Omotola Odutola, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Advertisement

Ana dai zargin matashin da tu’ammali da ƙwayoyi.

Karancin Masara Na Neman Durkusar Da Kiwon Kaji A Kasar nan.

Kanin wanda ake zargi da kashe mahaifiyar tasu, wanda yake aikin gadi, shi ya sanarwa makwaɓtansu abin da ke faruwa lokacin da ya dawo ya samu gawar mahaifiyarsu a kwance.

Advertisement

Samson wanda ya kasance ba ya gida na tsawon shekaru, ya dawo ne domin yin bikin babbar Sallah tare da mahaifiyarsa makonni biyu da suka wuce.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa an kama matashin ne bayan da makwaɓtansu suka gano cewa shi ya kashe mahaifiyar tasa, inda daga nan aka miƙa shi hannun ƴan sanda.

Advertisement

Kakakin ƴan sandan jihar ta Ogun, Omotola Odutola ta ce matashin yana da lalura ta kwakwalwa.

Ta kuma ce an kasance ana ɗaure lokuta da dama domin kada ya ji wa kansa ko mutane ciwo.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending