Connect with us

News

SUDAN:Makaman roka sun kashe ‘farar- hula 16’ a Sudan

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Akalla farar-hula 16 ne suka rasu bayan makaman roka sun fada kan gidajensu a yammacin Darfur na Sudan, kamar yadda wata kungiya ta lauyoyin yankin ta bayyana a ranar Asabar.

Yankin mai girma, wanda tuni yaki ya daidaita a farkon shekarun 2000, ya fuskanci rikice-rikice mafi muni tun a tsakiyar watan Afrilu a tsakanin janarorin Sudan biyu masu adawa da juna.

Bakuwar Tsutsa Ta Kori Mazauna Unguwar Gayawa Gandu Daga Gidajensu A Kano

“A lokacin musayar wuta ta hanyar makamin roka tsakanin sojojin kasar da kuma dakarun RSF, farar-hula 16 suka rasa ransu a ranar Juma’a, kamar yadda wata kididdiga ta wucin-gadi a Nyala ta bayyana,” in ji kungiyar.

Haka kuma maharbin boye ya kashe akalla mutum daya, kamar yadda kungiyar ta kara da cewa.

A El Geneina babban birnin Yammaci Darfur, a kusa da Chadi, rahotanni sun ce maharban boye sun ta kokarin harbin mazauna gida daga saman kwanon gidaje tun bayan da aka soma yakin, haka kuma dubban mutane sun tsere inda suka tsallaka iyaka.

Advertisement

Yakin, wanda ya barke a babban birnin Sudan a ranar 15 ga watan Afrilu sa’annan ya bazu zuwa Darfur duk a cikin watan, ya yi sanadin mutuwar akalla mutum 3,000 a fadin Sudan, kamar yadda aka kiyasta.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending