News
Jam’iyyar NNPP Ta Nemi Amurka Da EU Da Kuma AU Su Kawo Mata Dauki Kan Zaben Gwamnan Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jam’iyyar NNPP, ta nemi kasashen Amurka, Tarayyar Turai (EU) da Tarayyar Afirka (AU) su shiga tsakani kan shari’ar gwamnan Kano, inda ta danganta shari’ar a matsayin magudin hukuncin kotu domin kwace nasarar da Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya samu.
Leadership ta ruwaito cewa A zanga-zangar da aka gudanar a ranar Laraba a ofisoshin jakadancin Amurka, Tarayyar turai da tarayyar kasashen Afirka a Abuja, mukaddashin shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Abba Kawu Ali, ya ce, Kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zaben jihar ta yanke, don haka, kotun ta nuna cewa, gwamna Yusuf ne ya lashe zaben da aka yi a ranar 18 ga watan Maris.
Mutane mu Suna Cikin Mawuyacin Hali -Kakakin majalisar wakilan Nijeriya
Ya kara da cewa, manufar zanga-zangar da jam’iyyar NNPP ta gudanar a ofisoshin jakadancin, ita ce ta sanar da dukkanin kasashe da kungiyoyi masu kishin Dimokuradiyy halin da kotunan zabe ke ciki a Nijeriya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
