News
Hukumar Karbar Korafe-korafe Ta Kama Jami’an Tsaro Da Ake Zargi Da Badakalar Filaye A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano PCACC, ta kama waɗanda ke da hannu cikin almundahanar filaye, da suka hadar da jami’an tsaro da wasu jami’an gwamnati.
Shugaban hukumar Barrister Muhyi Magaji Rimingado, ne ya sanar da hakan, yayin wani taron tuntuba da hukumar ta gudanar a ranar Talata.
Gwamna Fintiri Ya Sanar Da Kirkirar Sabbin Masarautu 7 A Adamawa
Rimingado, ya ce an samu nasarar cafke wadanda ake zargin ne bisa aikin hadin gwiwa tsakanin hukumar da jami’an tsaro da ma’aikatar kasa da jami’an ma’aikatar sharia da na kotu, inda ya bayyana kokarin da hukumar ke yi wajen ganin an hukunta duk wanda aka samu da hannu a irin wannan badakala.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
