News
Nyesom Wike Ya Kwace Filin Buhari, Abbas, Akume Da Wasu Mutane 756 A Abuja
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike ya kwace filaye mallakar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas; da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume.
Haka kuma, dana wasu fitattun mutane 759 a Maitama II, Abuja. Haka kuma sokewar ta shafi rashin biyan takardar shaidar zama.
A cikin wata sanarwa daban, ministan ya ba da gargadi mai ƙarfi ga wasu masu filaye, ciki har da shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai Kingsley Chinda, tsofaffin shugaban majalisar dattijai Iyorchia Ayu da Ameh Ebute, da Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Tahir Monguno, da sauran mutane 610.
An ba su wa’adin makonni biyu don biyan kuɗin da ake bin su ba shi ko kuma za su fuskanci matakin soke filin nasu kamar yadda aka yi wa wasu.
