News
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Kan Korar Ma’aikata 127
Kungiyar Ƙananan Likitoci ta Najeriya (NARD), reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, ta ce za ta shiga yajin aikin gargadi na kwanaki uku daga yau Talata, domin nuna rashin jin daɗinta kan korar ma’aikatan lafiya 127 da hukumar kula da ma’aikatan Abuja (FCTA) ta yi.
Kungiyar Likitoci ta yanke shawarar shiga yajin aikin ne bayan wani taron gaggawa da ta gudanar a Asibitin Asokoro a ranar Litinin, kamar yanda Jaridar DAILY TRUST ta ruwaito.
An Kashe Sama Da Mutane 1,700 A Rikicin Iyakoki Da Muhalli A Najeriya — RAHOTO
Shugaban ƙungiyar, Dr George Ebong, ya bayyana matakin da hukumar FCTA ta dauka a matsayin “maras tushe kuma rashin imani.” Ya ce dole ne a gaggauta dawo da ma’aikatan bakin aiki tare da biyansu albashin watan Afrilu da aka dakatar.
“Wannan korar ba ta da wani dalili na kwarai kuma tana nuna yadda ake raina ma’aikatan lafiya. Ba za mu yarda da hakan ba,” in ji Dr. Ebong.
Ya kuma bukaci shugaban hukumar kula da ma’aikatan Abuja, Emeka Ezeh, da ya sauka daga mukaminsa saboda yadda aka tafiyar da al’amarin.
Kungiyar ta yi gargaɗi cewa idan Ministan Abuja, Nyesom Wike, bai dauki matakin da ya dace cikin kwanaki uku ba, to za su shiga yajin aikin sai baba ta gani, wanda hakan na iya haddasa durƙushewar harkokin lafiya a babban birnin tarayya.
-
News3 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News5 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
