Connect with us

News

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibin jami’a

Published

on

Yan bindiga

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Rundunar ƴan sanda ta jihar Cross River ta tabbatar da sace wani ɗalibin jami’ar Arthur Jarvis da ke Akpabuyo a kusa da Calabar.

Advertisement

 

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Irene Ugbo ce ta tabbatar da faruwar lamarin a wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai Ƙasa, NAN ta wayar tarho a yau Laraba a Calabar.

Advertisement

Dalilin Da Manyan Kungiyoyin Turai Ba Sa Son Sayen Ronaldo

Ɗaliban na tsaka da komawa ɗakunansu ne daga inda suka je karatu, sai kawai ƴan bindiga suka far musu da misalin karfe 8 na dare a jiya Talata.

Advertisement

 

Yayin da ƴan bindigar suka kama ɗaya daga cikin ɗaliban, wasu kuma da suka gudu domin tsira da rayukansu, sun samu raunuka daban-daban.

Advertisement

 

Misis Ugbo ta ce kwamishinan ‘yan sanda, Aminu Alhassan, ya shirya dakarun yaƙi da garkuwa da mutane da su dakile yunƙurin karya doka da oda da kuma tabbatar da kuɓutar da dalibin da aka sace.

Advertisement

 

Ta ce ‘yan sanda sun fara bincike kan lamarin.

Advertisement

 

Mukaddashin magatakardar jami’ar, Ngozi Ughas, a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce shugabannin jami’ar sun tashi tsaye kan lamarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending