News
El-Rufai ya bada hutun kwana biyu a Kaduna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin jihar Kaduna ta bada hutun kwana biyu saboda mutanen jiha su garzaya ofisoshin zaɓe su yi katin zaɓe.
Hakan na kunshe ne a wata takarda wanda babban mai bashi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye ya fitar ranar Talata.
KAROTA ta cafke wasu matasa da makamai da kayan-maye a kano
” Gwamnatin Kaduna ta bada hutun kwanaki biyu, ranar Laraba da Alhamis domin waɗanda ba su da katin zaɓe su garzaya ofishin INEC su yi.
” Haka kuma gwamnatin ta umarci masu kamfanoni da su ɗaga wa ma’aikatan su kafa suma su je su yi katin zaɓen.
Dama kuma idan ba a manta ba a jihar Kaduna ranar Juma’a hutu ce, saboda haka duk mai bukatar sabonta katin zaɓe ga dama ta samu.
A cikin sanarwar, gwamnati ta umarci mutane da su tabbata sun killace katunan su na zaɓe domin da shine za su samu damar kaɗa kuri’a idan zaɓr ya zo.
Channel
-
News1 day ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News4 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
