Connect with us

News

ECOWAS ta gargadi ma’aikatanta a Najeriya kan matsalar tsaro

Published

on

Shugaba Muhammadu Buhari da tambarin ECOWAS

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar gudanarwar kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ta shawarci dukkanin jami’ai da ma’aikatanta da su yi taka-tsan-tsan tare da kiyayewa kan duk wasu wurare da hanyoyi da suke bi saboda halin tsaron da ake fama da shi a fadin Najeriya a yanzu.

 

Advertisement

A wata sanarwa hukumar ta bayyana cewa bayanan sirri sun yi gargadin cewa akwai shirin da bata-gari ke yi na shiga sassan kasar musamman manyan biranen jihohi, da suka hada da babban birnin tarayya Abuja domin aikata miyagun ayyuka.

Tsaro: ’Yan Najeriya Sun Fara Kare Kansu Da Kansu —Monguno

Advertisement

Ayyukan da suka hada da satar mutane domin karbar kudin fansa da kuma daukar sabbin mabiya domin gudanar da ayyukan ta’addanci.

 

Advertisement

Hukumar ta bayar da wasu shawarwari na tsaro ga jami’an nata kan yadda za su gudanar da harkokinsu a duk inda suke domin kauce wa fadawa cikin matsalar tsaron.

 

Advertisement

Sai dai ta bukaci da kada su tayar da hankali tana mai ba su tabbacin cewa hukumomin tsaron Najeriyar na yin duk abin da ya kamata kan kalubalen.

 

Advertisement

 

BBC HAUSA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending