Connect with us

News

Sojoji Sun Kwato Mutum 6 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dakarun sojin Najeriya sun kubuto mutane 6 da ‘yan bindiga su ka yi garkuwa da su a jihar Kaduna.

Advertisement

 

Dakarun sun kubutar da mutanen ne a yayin wani aikin sintiri da suke yi a yanki Kagon Kadi da ke karamar hukumar Chikun ta jihar.

Advertisement

 

Majalisa Na So A Gaggauta Shari’ar Barayin Man Fetur

Advertisement

Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida na jihar Samuel Aruwan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya sa wa hannu a ranar Litinin, a garin Kaduna.

 

Advertisement

Kwamishinan ya ce, daga bayanan da ya ke samu daga filin daga, sojojin da ke sintiri, sun bude wuta kan ‘yan bindigan ne a kokarin da su ke yi na kakkabe ‘yan bindigan da su ke boye a dazukan Kagon Kadi da Labi, da kuma bakin Kogin Udawa.

 

Advertisement

’Yan bindigan sun tsere sakamakon fin karfinsu da sojojion suka yi, a inda su ka bar wasu mutane 6 da su ke garkuwa da su a sansaninsu.

 

Advertisement

Sanarwar ta ce gwamnan jihar, Nasir El-Rufa’i ya yi murna tare da jinjina wannan kokari na dakarun sojin.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

‘DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending