Connect with us

News

Sace Dalibai: Gwamnati Ta Bude Makarantu 45 Da Ke Rufe A Zamfara

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

Ma’aikatar Ilimi ta Zamafara, ta ce gwamnatin jihar  ta ba da umarnin bude makarantu 45 da a baya tabarbarewar tsaro ya sa aka rufe su.

Sakataren ma’aikatar, Kabiru Attahiru ne ya bayyana hakan a Gusau, yayin da yake karbar jami’an sashen Fasaha na Ilimi a jihar (EiE), yayin ziyarar ban girma da suka kai ma’aikatar.

Gwamnatin jihar ta rufe makarantun ne a watan Satumbar 2021, bayan sace daliban Makarantar Gwamnati ta Kaya da ke Karamar Hukumar Maradun da ’yan bindiga suka yi.

“Mun raba bude makarantun zuwa kashi uku, inda muka ba su suna da launi, wato kore, da kawaya, da kuma ja.

“Masu alamar kore su ne muka bude yanzu, kuma suke a wuaren da ba a fuskantar barazanar tsaro.

“Sai masu launin rawaya da ke fuskanta ’yar karamar barazana, sannan sai jajaye da suke fuskantar babban kalubalen tsaron.

Advertisement

“Yanzu dai jimillar makarantu 30 ne kadai ke rufe, amma muna fatan a kara samun ingantar harkokin tsaro domin su ma mu bude su baki daya”,  inji shi.

 

 

 

 

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending