News
Sace Dalibai: Gwamnati Ta Bude Makarantu 45 Da Ke Rufe A Zamfara
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN
Ma’aikatar Ilimi ta Zamafara, ta ce gwamnatin jihar ta ba da umarnin bude makarantu 45 da a baya tabarbarewar tsaro ya sa aka rufe su.
Sakataren ma’aikatar, Kabiru Attahiru ne ya bayyana hakan a Gusau, yayin da yake karbar jami’an sashen Fasaha na Ilimi a jihar (EiE), yayin ziyarar ban girma da suka kai ma’aikatar.
Gwamnatin jihar ta rufe makarantun ne a watan Satumbar 2021, bayan sace daliban Makarantar Gwamnati ta Kaya da ke Karamar Hukumar Maradun da ’yan bindiga suka yi.
“Mun raba bude makarantun zuwa kashi uku, inda muka ba su suna da launi, wato kore, da kawaya, da kuma ja.
“Masu alamar kore su ne muka bude yanzu, kuma suke a wuaren da ba a fuskantar barazanar tsaro.
“Sai masu launin rawaya da ke fuskanta ’yar karamar barazana, sannan sai jajaye da suke fuskantar babban kalubalen tsaron.
“Yanzu dai jimillar makarantu 30 ne kadai ke rufe, amma muna fatan a kara samun ingantar harkokin tsaro domin su ma mu bude su baki daya”, inji shi.
DAILY TRUST
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
