Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

Published

on

yan bindiga sun sace mutane

Rahotanni sun bayyana cewa, wasu ‘yan bindiga dauke da makamai karkashin jagorancin wani fitaccen kasurgumin dan bindiga mai suna Babaro sun kwace iko da jagorancin karamar hukumar Kankara a jihar Katsina.

Wani mai sharhi kan harkokin tsaro, Bakatsine ne ya bayyana hakan a wani sharhi da aka wallafa a shafinsa na X, yana mai cewa, maharan sun kashe mazauna yankin da dama, tare da hana ayyukan noma, da kuma haddasa durkushewar ayyukan kasuwanci na yau da kullum a yankin.

Advertisement

Dalibai 4 Cikin 10 Na Ta’ammali Da  Miyagun Ƙwayoyi – NDLEA

“Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan bindiga karkashin jagorancin babaro sun kwace iko da jagorancin karamar hukumar Kankara, jihar Katsina. An hana noma daga Marabar Kankara zuwa ‘Yantumaki, an kashe mutane da dama, an yi garkuwa da wasu, kiwon lafiya ya durkushe. Mazauna garin suna rokon Gwamna @dikko_radda da gwamnatin tarayya (FG) su kawo musu dauki cikin gaggawa.” in ji sanarwar

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, karamar hukumar Kankara na ci gaba da kasancewa ramin kura, inda hare-haren yankin ya jawo fargaba a fadin kasar, musamman ma sace yara dalibai sama da 300 a watan Disambar 2020.

Advertisement

Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, gwamnatin jihar Katsina ko hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance dangane da wannan rahoton ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending