Connect with us

News

Rikici Ya Sa Mutum 9,000 Hijira Kudancin Sudan —MDD

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa sama da mutum 9,000 rikici ya daidaita a baya-bayan nan a yankin Kudancin Sudan.

Advertisement

 

Majalisar ta ce a halin da ake ciki, sansanin ’yan gudun hijira da ke Malakal ya batse da sabbin ’yan gudun hijira daga Kudancin Sudan.

Advertisement

Kotu Ta Tsare Matashi A Kurkuku Kan Zargin Fyade

 

Bayanai sun nuna hare-hare sun tilasta wasu mazauna yankin buya a cikin fadamu da dazuzzuka don tsira da ransu.

Advertisement

 

A cewar Majalisar, ba a kai ga tantance adadin wadanda suka mutu da wadanda aka yi wa fyade ba saboda kazancewar rikicin yankin.

Advertisement

 

 

Advertisement

Kazalika, an samu rahotanni da dama dangane da sace mutane da yawan gaske a yankin, in ji MDD.

 

Advertisement

Rahotanni sun ce, kaso 75 cikin 100 na sabbin ’yan gudun hijirar, mata ne da kananan yara.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending