Connect with us

News

Mutum 4 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Neja

Published

on

Hatsarin Mota

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

Mutum hudu ne suka riga mu gidan gaskiya sannan uku sun jikkata a hatsarin motar da ya auku ranar Lahadi a Jihar Neja.

Advertisement

Hatsarin a cewar Kwamadan Hukumar Kiyaye Hadurra reshen jihar, Kumar Tsukwam, ya auku ne da daddare kusa da kauyen Nami da ke Karamar Hukumar Agaie ta jihar.

Sojojin Najeriya sun fatattaki gungun ‘yan ta’adda a Zurmi

Ya ce motar da lamarin ya shafa, ta dauko kayan sunadarai ne da kuma fasinjoji 49 daga Legas da nufin zuwa Kano.

Advertisement

“Mutum 49 (duka maza) hatsarin ya ritsa da su inda hudu suka mutu nan take, uku sun jikkata sannan 42 sun tsallake rijiya da baya.

“An kwashi wadanda suka ji rauni da ma gawarwakin zuwa Babban Asibitin Lapai,” in ji Tsukwam.

Advertisement

Ya ce hatsarin ya auku ne sakamakon gudun wuce kima da direban motar ya yi wanda hakan ya sa motar ta kwace masa ta fadi.

(NAN)

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending