Politics
Jam’iyyar PDP tace babu Wani Koma Baya Kan Rashin Amincewa Da Bukatarmu A Gaban Kotu
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jam’iyyar PDP ta ce kin amincewa da bukatar da ta yi na nuna yadda ake shari’ar karrakin zaben shugaban kasa kai tsaye ba wani koma-baya ba ne.
Idan za’a iya tunawa a jiya ne kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa ta ki amincewa da bukatar dan takarar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar daken a rika nuna zaman kotun kai tsaye.
Da yake magana da manema labarai bayan kotun ta yanke hukuncin, lauyan PDP, Eyitayo Jegede ya ce maimakon su tsaya kan kin amincewa, jam’iyyar da dan takararta a shirye suke don kan rahoton share faga gabanin sauraron karar.
Dangane da hade dukkan koke-koke na kalubalantar zaben Bola Tinubu, Jegede ya ce dokar kasa ce ta tilasta batun, don haka ba su da wata adawa a kai.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
